Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bukaci matasan kasar sa da su rika shiga harkokin al'umma a matakin farko, domin fadada fahimtar su game da yanayin kasar da al'ummar ta, su kuma yi amfani da kwazon su wajen kirkiro sabbin abubuwa, da sana'o'i masu alfanu ga kasa.
Shugaban na Sin wanda ya bayyana hakan cikin wata wasika ta martani, ga sakon wani dalibi da ya shiga shirin kirkirar sana'o'i, karo na uku na kasar Sin mai lakabin "Internet Plus", ya ce yana fatan dalibai za su karfafa zukatan su, su kuma zage damtse wajen cimma burikan da kasar su ta sanya gaba.(Saminu Alhassan)