in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in MDD ya yi Allah wadai da harin ta'addanci a Burkina Faso
2017-08-15 09:25:45 cri
Sakatare janar na MDD Antonio Guterres, a ranar Litinin yayi Allah wadai da harin ta'addanci da aka kaddamar a Ouagadougou, babban birnin kasar Burkina Faso, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 18.

Mista Guterres ya ce, babu wata takamammiyar hujja na aikata irin wadannan abubuwa na cin zarafin bil adama. Ya jaddada aniyar MDD wajen tallafawa Burkina Faso a kokarinta na yaki da ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi.

Mai magana da yawun sakatare janar din Farhan Haq, ya ce, sakataren ya nanata aniyarsa ga kasashen G5 na yankin Sahel, sakamakon kalubalolin tsaro da suke fuskanta ta yadda za'a taimaka musu wajen samun dauwamamman zaman lafiya da cigaban yankin.

Kasar Faransa da wasu kasashen Afrika 5 da suka hada da Burkina Faso, Chad, Mali, Mauritania da Nijer, a watan da ya wuce suka cimma matsaya na kaddamar da runduna ta musamman mai yaki da 'yan tada kayar baya masu tsattsauran ra'ayi a yankin Sahel. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China