in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane a kalla 3 sun mutu sakamakon harin ta'addanci da aka kai a Ouagadougou
2017-08-14 13:49:46 cri
A jiya da dare ne, aka kai wani harin ta'addanci a Ouagadougou, babban birnin kasar Burkina Faso, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane a kalla 3, yayin da sama da mutane 10 kuma suka ji rauni, amma har yanzu ba a tabbata da asalin mutanen da suka mutu ba.

Rundunar 'yan sandan Burkina-faso ta sanar da cewa, an kai hari da bindigogi a kan wani titi dake tsakiyar birnin Ouagadougou, sai dai sojojin tsaro sun riga sun isa wurin, kana sun killace yankunan dake dab da wurin. Haka kuma 'yan sandan sun yi kira ga mazauna wurin da su kai zuciya nesa, su kuma zauna a gidajensu, kana su nisanci wuraren dake kusa da tsakiyar birnin.

Wasu mazauna wurin sun ce, an kai farmakin ne a wani dakin shan kofi dake kan titin, kana an ji karar bindiga da abubuwan fashewa a duk tsawon daren ranar, sai dai har yanzu jami'an tsaro sun killace wurin.

Kasar Burkina Faso dake yammacin nahiyar Afirka ta yi iyaka da kasar Mali daga bangaren arewacin kasar, kana a 'yan shekarun kasar ta fuskantar harin ta'addanci. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China