Kawo yanzu mahukuntan lardin Sichuan na kasar Sin, sun tabbatar da rasuwar mutane 9, tare da jikkatar wasu 164, sakamakon girgizar kasa mai karfin maki 7.0, wadda ta auku a garin Zhangzha dake gundumar Jiuzhaigou a daren jiya Talata.
Tuni dai shugaban kasar Sin Xi Jinping da firaministan kasar Li Keqiang, suka ba da umarnin hanzarta daukar dukkanin matakan da suka wajaba na tallafin jin kai, a yankin da wannan bala'i ya auku.