in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a sa lura ga yanayin kananan yara a Congo Kinshasa
2017-08-08 16:01:08 cri
Asusun kananan yara na MDD ya bayar da wata sanarwa a jiya Litinin, wadda ke cewa, kamata ya yi bangarori daban daban su mai da hankali, ga yanayi mai tsanani da kananan yara da iyalansu suke fuskanta a yankin Grand Kasai dake kasar Congo Kinshasa.

Daraktar ofishin asusun dake yankin yammaci da tsakiyar nahiyar Afirka Marie Pierre Poirier, ta jaddada a cikin sanarwar cewa, tilas ne bangarori daban daban da rikicin ya shafa, su tabbatar da kiyaye hakkin kananan yara, da kare su daga cin zarafi, da tabbatar da tsaron makarantu da hukumomin kiwon lafiya, da amincewa ma'aikata masu aikin jin kai samar da gudummawa ga jama'a, ba tare da fuskantar wasu matsaloli ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China