in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta kudu ta yaba da shirin bunkasa masana'antu na kungiyar BRICS
2017-08-01 10:11:39 cri
Ministan ciniki da masana'antu na kasar Afrika ta kudu Rob Davies, ya ce za a iya amfani da matakin bunkasa ayyukan masana'antu da kungiyar kasashe masu samun ci gaba cikin sauri wato BRICS ta dauka, a matsayin wata hanya ta samun ci gaba tare da samar da guraben aikin yi.

Kungiyar BRICS ta amince da shirin mai manufofi 7 ne yayin taron yini biyu na ministocin ciniki da masana'antu na kasashe mambobinta da ya gudana karshen makon da ya gabata a Hangzhou na kasar Sin.

Munufofin shirin na bunkasa hadin gwiwa a bangaren masana'antu tsakanin kasashe mambobin kungiyar su hada da: karfafa hadin kai ta fannonin ayyukan masana'antu tare da tsarawa da gama dabarun wuri guda da inganta sabbin kayayyakin aikin masana'antu da fadada hadin gwiwa a fannin bunkasa fasaha da kirkire-kirkire, da kuma kanana da matsakaitan sana'o'i.

Rob Davies ya ce shirin zai bada dama ta samu tare da musayar sabbin fasahohi ta hanyar samun jari daga kasashen waje, tare da gina karfin yin takara da sauran kasashen duniya. (F"aiza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China