in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi tir da harba makami mai Linzami mai karfin kai wa wata nahiya da kasar Korea ta Arewa ta yi
2017-07-29 12:41:07 cri

Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi tir da harba makami mai linzami mai nisan zango dake da karfin kaiwa wata nahiya, da Jamhuriyar Demokuradiyyar al'ummar Korea ta yi.

Wata sanarwa da mataimakin kakakin MDD Farhan Haq ya fitar jiya, ta ruwaito Antonio Guterres na cewa, harba makamin sake take dokokin kwamitin sulhu na majalisar ne.

Sanarwar ta ce dole ne shugabancin kasar ta yi cikkaken biyayya ga dokokin kasa da kasa tare da yin aiki da al'ummomin kasashen waje domin warware matsalolin da suka shafi zirin Korea.

Sakatare Janar din ya jadadda yin kira ga shugabancin Jamhuriyar Demokuradiyyar al'ummar Korea, ta mai da martini ga bukatar Jamhuriyar Korea, ta sake bude hanyoyin sadarwa musammam tsakanin rundunonin soji domin rage rashin fahimta da fargaba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China