in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar IOC ta tsaida kudurin zabar biranen da za su dauki bakuncin gasar wasannin Olympics ta shekarar 2024 da ta 2028
2017-07-20 10:22:30 cri
Hukumar wasannin Olympics ta duniya wato IOC, ta gudanar da cikakken zama na 130 a birnin Lausanne dake kasar Switzerland a kwanakin baya, inda aka jefa kuri'u, tare da tsaida kudurin zabar biranen da za su dauki bakuncin gudanar da gasar wasannin Olympics ta shekarar 2024 da ta 2028 a sa'i daya, za kuma a tsaida kudurin baiwa ko dai birnin Los Angels ko Paris, damar karbar bakuncin gudanar da gasar wasannin Olympics, a cikakken zama na 131 na hukumar IOC da za a gudanar a birnin Lima dake kasar Peru a watan Satumba na bana.

Membobi 83 sun halarci cikakken zama a wannan karo, inda suka amince da zartas da kudurin da kwamitin gudanarwa na hukumar IOC ya gabatar a watan da ya gabata, wato yadda daya daga cikin birane biyu da suke neman daukar bakuncin gasar wasannin Olympics ta shekarar 2024 zai cimma nasarar samun izinin, yayin da dayan zai samu iznin daukar bakuncin gudanar da gasar wasannin Olympics ta shekarar 2028. Da wannan mataki za a cimma dacewa da moriyar wasannin Olympics a dogon lokaci.

Ana dai daukar wannan sakamako a matsayin nasarar da shugaban hukumar IOC Thomas Bach ya samu, domin membobin hukumar sun ki amincewa da shawarar da ya gabatar karon farko da ya bayyana ta a farkon shekarar bana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China