in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta warware kararraki 1,800 da suka jibanci kutsen muhimman bayanan jama'a
2017-07-18 10:44:59 cri
Ma'aikatar tsaron jama'a ta kasar Sin ta bayyana cewa,daga watan Maris zuwa wannan lokaci rundunar 'yan sandan kasar ta yi nasarar warware kararrakin da suka shafi kutse a muhimman bayanan jama'a da masu satar shiga intanet ke aikatawa.

Bayyana muhimman bayanan jama'a dai ya sabawa dokar kasa, kuma aya ta 111 ta dokar kasar Sin ta bayyana cewa, wajibi ne a kare muhimman bayanan jama'a dake zaune a cikin kasar gami da hakkokinsu kamar yadda doka ta tanada.

A watan Mayun wannan shekara ce dai, kotunan kasar Sin suka yanke wani hukunci mai tsauri, dake cewa, duk wadanda aka kama da samu ko sayar da muhimman bayanai 500 ko sama za su fuskanci daurin da ya kai shekaru 7 a gidan yari.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China