in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jarin da kasar Sin ta zuba wa kasashen waje ya ragu
2017-07-14 11:10:56 cri
Alkaluman da hukumomin kasar Sin suka fitar ya nuna cewa adadin jarin da kasar Sin take zubawa kasahsen waje a kai tsaye wato (ODI) ya ragu da kashi 45.8 bisa 100 zuwa dala biliyan 48.19 cikin watanni shida na wannan shekara.

Kwamfanonin kasar Sin sama da 3,900 sun zuba jari a kasashen waje 145 da sassa daban daban na duniya daga watan Janairu zuwa watan Yuni, kamar yadda ma'aikatar kula da al'amurran ciniki ta kasar Sin ta tabbatar da hakan.

An samu raguwar ne sakamakon sauye sauyen manufofin tattalin arzikin da kasar Sin ke gudanarwa da nufin inganta shi, bisa la'akari da yanayin da ake ciki na rashin tabbas a kasashen ketare, da kuma matakan da gwamnati ke dauka domin dakile hanyoyin zuba jari marasa tabbas, in ji kakakin ma'aikatar cinikin ta Sin Gao Feng.

Gao ya ce, a tsakiyar wannan shekara, tattalin arzikin Sin na cigaba da karuwa yadda ya kamata, hakan ya karfafa gwiwar Sinawa masu zuba jari suka yanke shawarar barin jarinsu a cikin gida.

Matsalar karuwar tashe tashen hankula a kasa da kasa da shiyya, da hare haren ta'addanci da tsauraran dokokin kasuwanci a wasu kasashen duniya su ma wasu dalilai ne da suka haifar da mummunan tasiri ga aikin zuba jari a ketare a watannin shidan farkon wannan shekarar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China