in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar sojin ruwa ta Najeriya ta gargadi jami'anta game da kafofin sadarwa na zamani
2017-07-16 12:57:13 cri
Hukumomin kula da sojin ruwa ta Najeriya NN ta yi gargadi game da wallafa duk wani abu dake da nasaba da ayyukanta a shafukan sada zumanta na zamani.

Rear Admiral Victor Adedipe, kwamandan hukumar sojin ruwa ta shiyyar gabashin kasar (FOC), shi ne yayi wannan gargadi a sansanin hukumar ta NNS Jubilee Base a kudancin jahar Akwa Ibom.

Ya ce kasancewar da yawa daga cikin jami'an rundunar suna cikin wasu kungiyoyi na shafukan sada zumunta na zamani wanda ya shafi na dangi ko abokai, amma ya hore su da su yi taka tsantsan game da irin abubuwan da zasu wallafa a shafukan.

Adedipe ya ce, a kwanannan an fitar da sabon tsari na ka'idojin da suka shafi mu'amala da kafafen sada zumunta na zami, ya ce ya kamata kowa ya neme su domin karantasu.

Babban jami'in sojin ruwan ya bukaci jami'an su kiyaye ka'idojojin hukumar da suka shafi yin ta'ammali da kafofin sadarwa na zamani.

Ya ce wallafa duk wani batu da ya shafi ayyukan hukumar a shafukan sada zumuntar zai iya samar da muhimman bayanai ga bata gari.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China