in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin saman Najeriya ta fara horas da dakaru aiki sarrafa jirage marasa matuka
2017-07-13 10:07:34 cri
Rundunar sojin sama ta tarayyar Najeriya ta fara horas da dakarun ta dabarun sarrafa jirage marasa matuka, a wani mataki na inganta ayyukan tsaro, da shawo kan sabbin kalubale da ake fuskanta a fannin.

Rundunar ta NAF ta ce a shekarar 2013 aka fara aiwatar da wannan horo, amma daga baya aka dakatar saboda karancin kayan gyaran nau'in wadannan jirage, kafin kuma yanzu a sake bude gudanar da shi.

Da yaka karin haske game da hakan, yayin kaddamar da bada horon a jihar Kaduna dake arewacin Najeriya, babban jami'i mai lura da tsare tsare AVM Iliyasu Muhammad, ya ce cibiyar bincike da samar da ci gaba ta rundunar, ta riga ta samar da managarcin tsarin ba da wannan horo, a wani mataki na tabbatar da dorewar sa. Za kuma a fara ne da horas da dakaru 5 cikin watanni 3.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China