in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan kara yin hadin gwiwa da Equatorial Guinea game da shawarar ziri daya da hanya daya
2017-07-13 19:42:14 cri

Shugaban majalisar ba da shawara kan harkokinn siyasa na kasar Sin Yu Zhengsheng ya bayyana cewa, kasashen Sin da Equatorial Guinea za su kara yin hadin gwiwa karkashin shawarar ziri daya da hanya daya.

Mr. Yu wanda har ila yau shi ne shugaban kwamitin taron tuntuba game da harkokin siyasa na kasar Sin, ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da mataimakin shugaban kasar Equatorial Guinea Teodoro Nguema Obiang Mangue.

A nasa jawabin Mangue ya yaba wa kasar Sin bisa taimakon da ta dade tana baiwa kasarsa. Kana a shirye kasarsa take ta kara zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin ta yadda hakan zai amfana wa al'ummomin kasashen biyu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China