in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta kaddamar da aikin hakar manta a hukumance
2017-07-07 09:58:01 cri
A ranar Alhamis shugaban kasar Ghana ya kaddamar da filayen man kasar Ghana ta uku wadda aka fi sani da Sankofa- Gye Nyame, inda za su fara hako man a kasuwa.

Yankin dake da albarkatun man wato (OCTP), ya kunshi yankin da ake saran samar da man wanda ya kai ganga 45,000 a kowace rana, da kuma iskar gas wanda ya kai cubic mita miliyan 171 a kullum wanda ake saran fara aikinsa a shekarar 2018.

Shugaban na Ghana ya ce, abokan hulda masu zuba jari sun nuna sha'awarsu na gudanar da aikin duk da rashin tabbas din da ake da shi sakamakon karyewar farashin danyen man a kasuwannin duniya.

Akufo-Addo ya ce suna cigaban da daukar matakan da suka dace domin tabbatar da ganin kasar Ghana ta zama babbar cibiyar samar da man fetur a yammacin Afrika. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China