in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Angola ta jinjinawa kasar Sin game da taimakon da take bata wajen raya tattalin arziki
2017-07-14 09:37:20 cri
Mataimakin shugaban kasar Angola Manuel Domingos Vicente ya ce kasarsa na yabawa kasar Sin game da goyon bayan da take ba ta,wajen sake farfadowa da raya tattalin arziki.

Manuel Vicete ya yi wannan jawabi ne jiya a birnin Luanda, lokacin da yake ganawa da dan majalisar gudanarwar Sin kuma Ministan tsaron kasar Chang Wanquan dake ziyara a kasar.

Mataimakin shugaban kasar ya ce kasashen biyu na amfana da ingantaccen tubalin dangantaka dake tsakaninsu, wanda ya ce yana da muhimmanci wajen dorewar zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

Ya ce Angola ta dauki shawarar 'ziri daya da hanya daya' da kasar Sin ta gabatar da matukar daraja, kuma a shirye take ta hada hannu da kasar karkashin shirin, domin samun ci gaba na bai daya ta yadda al'ummomin kasashen biyu za su amfana.

A nasa bangaren, Chang Wanquan ya ce makasudin ziyarar ta sa shi ne, aiwatar da muhimmin mataki da shugabannin kasashen biyu suka cimma, domin inganta hadin kai a dukkan bangarori, ciki har da tsaro, tare da daukaka huldar dake tsakaninsu zuwa wani mataki. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China