in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kafa sansanin sojojin Sin a Djibouti
2017-07-11 20:15:53 cri
A yau Talata ne a birnin Zhanjiang dake lardin Guangdong na kasar Sin, aka yi bikin tashin sojojin gwamnatin kasar Sin zuwa kasar Djibouti.

Kasar Sin ta tura sojojinta zuwa wani sansanin ba da tabbaci da kasar ta gina a kasar Djibouti, bisa kudurin da gwamnatocin kasar Sin da kasar Djibouti suka tsai da cikin hadin gwiwa. Wannan sansanin da aka gina a birnin Djibouti domin tabbatar da tsaron jiragen ruwa, kiyaye zaman lafiya da kuma ba da taimakon jin kai ga kasashen Afirka da yammacin Asiya, zai kuma ba da taimako wajen gudanar da atisayen sojoji, yin hadin gwiwar ayyukan soja da kuma ba da taimakon gaggawa a kasashen ketare da sauran ayyukan da abin ya shafa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China