in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Janyewar sojojin Indiya daga yankin kasar Sin, shi ne sharadin farko na yin tattaunawa a tsakanin Sin da Indiya
2017-07-10 20:27:30 cri
Kwanan baya ne, rahotanni ke nuna cewa, sojojin tsaron iyakar kasar Indiya da suka shiga cikin yankin kasar Sin ba tare da izini ba suka fara kafa tantunansu, a kokarin yin fito-na-fito da takwarorinsu na Sin na dogon lokaci.

Kasashen Sin da Indiya za su iya tuntubar juna ta hanyar diplomasiyya ko a'a? Ko za su ci gaba da warware batun ta hanyar diplomasiyya ko a'a? Game da batun, Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana yau Litinin a nan Beijing cewa, kasar Sin ta sake bukatar Indiya da ta janye sojojinta daga yankin kasar Sin a matsayin sharadi na farko, kana tushen da kasashen 2 za su tuntubi juna da yin tattaunawa a tsakaninsu. Kasar Sin na fatan Indiya za ta dauki hakikanin matakan da suka dace don warware wannan batu cikin ruwan sanyi. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China