in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta nuna adawar ta ga gwajin makamai masu linzami da koriya ta arewa ke yi
2017-07-04 19:02:57 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya ce gwamnatin Sin na adawa da gwajin makamai masu linzami da kasar koriya ta arewa ke yi.

Mr. Geng Shuang wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai, ya ce batun yanayin da ake ciki a zirin Koriya na da sarkakiya, don haka Sin ke fatan dukkanin sassan da batun ya shafa za su kai zuciya nesa, domin kaiwa ga magance dukkanin matsaloli, tare da tabbatar da tsarin zaman lafiya da lumana a zirin.

Manyan jami'an tsaron kasar Koriya ta kudu dai sun fidda wata sanarwa a Talatar nan, suna masu korafin cewa koriya ta arewa ta harba makami mai linzami a gabar ruwan gabashin yankin ta da ke kusa da Banghyeon, wanda ke arewa da birnin Pyongan, da misalin karfe 10 saura minti 20 na safiya bisa agogon yankin.

Daga bisani ita ma koriya ta arewan ta tabbatar da gwajin makamin wanda ke cin dogon zango, tana mai bayyana shi da wani gagarumin ci gaba a shirin ta na bunkasa makamai masu linzami.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China