in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fadar White House ta karyata yiwuwar ziyarar Trump zuwa Birtaniya
2017-07-04 10:11:13 cri
A ranar Litinin fadar White House ta Amurka ta yi watsi da wasu rahotanni dake nuna cewa shugaban kasar Donald Trump na shirin kai ziyarar aiki a Birtaniya.

An jiyo mataimakiyar sakataren hulda da 'yan jaridu ta fadar White House Sarah Huckabee Sanders, ta ambato cikin rahoton da jaridar New York Times ta wallafa cewa, babu wani shiri game da ziyarar shugaban na Amurka zuwa kasar Birtaniya cikin wannan watan.

A cewar fadar White House, Trump zai halarci taron koli na G20 ne a birnin Hamburg na kasar Jamus tsakanin ranakun Jumma'a da Asabar, kuma zai halarci bikin muhimmiyar ranar Bastille Day a birnin Paris na kasar France a ranar 14 ga watan Yuli. Trump ya yanke shawarar soke ziyarar tasa ne zuwa kasar Birtaniya, bisa fargabar da ake yi game da yiyuwar samun mummunar zanga zanga a kasar.

Firaiministan Birtaniya Theresa May ce ta gayyaci mista Trump don ziyarar aiki a Birtaniyan tun lokacin da ta ziyarci Washington a karshen watan Janairu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China