in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron PRC na kungiyar AU
2017-06-27 20:13:42 cri
A yau ne aka bude taron wakilin din-din-din na kungiyar tarayyar Afirka, a daidai lokacin da aka bude taron kolin kungiyar karo na 29 a birnin Addis Ababa na kasar Habasha.

Ana saran taron wakilan ya shirya ajandar taron kolin kungiyar inda za a gabatar da shawarwarin da ake fatan hukumar zartarwar kungiyar za ta amince da su, yayin zamanta a ranar 30 ga watan Yuni zuwa 1 ga watan Yuli, sai kuma taron shugabannin kasashe mambobin kungiyar wanda zai gudana daga ranar 3 zuwa 4 ga watan Yuli.

A cewar shugaban hukumar zartarwar kungiyar Moussa Faki Mahamat, taron kolin AU na bana zai mayar da hankali kan batutuwan zaman lafiya da tsaro da batun kaurar jama'a a nahiyar da sauransu. Sauran sun hada da abubuwan dake faruwa a kasashen Sudan ta kudu, Libya, Mali, Jamhuriyar Afirka ta tsakiya, Burundi, Jamhuriyar demokiradiyar Congo, da yankin Darfur da Somaiya da sauran muhimman batutuwa.

Taron kolin na bana dai zai gudana ne daga ranar 27 ga watan Yuni zuwa 4 ga watan Yuli.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China