in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin kasashen wajen Afirka na shirin ganawa a Kigali don tattauna yadda za a aiwatar da gyare-gyaren da AU ta gabatar
2017-05-05 09:41:04 cri
A ranar 7 ga watan Mayu ne ake saran ministocin harkokin wajen kasashen Afirka baki daya za su gana a birnin Kigali na kasar Rwanda, don tattauna yadda za a aiwatar da shirin gyare-gyaren da kungiyar tarayyar Afirka(AU) ta gabatar.

A yayin taron kungiyar ta AU karo na 27 da aka gudanar cikin watan Yulin da ya gabata a birnin Kigali ne, kasashe mambobin kungiyar suka dorawa shugaba Paul Kagame na kasar Rwandan nauyin jagorantar yadda za a aiwatar da gyare-gyaren da kungiyar ta gabatar, ta yadda kungiyar za ta cimma nasarar manufofin da ta sanya a gaba na inganta rayuwar al'ummomin nahiyar.

A watan Janairun ne dai dukkan shugabannin kasashe da gwamnatocin kungiyar suka amince da gyare-gyaren da kungiyar ta gabatar a yayin ganawarsu a birnin Addis Ababan kasar Habasha.

Wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen kasar Rwandan ta fitar ta bayyana cewa, shugaban kasar Paul Kagame zai karbi bakuncin taron ministocin harkokin wajen kasashen Afirka 54 da na jakadun kasashen Afirka da ke aiki a kungiyar AU domin tattauna hanyoyin da za a aiwatar da wadannan gyare-gyare.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China