Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya bayyana cewa, kasa daya tsarin mulkin biyu shi ne tsarin da ya dacewa wajen ci gaba da wanzar da zaman lafiya da mako mai kyau ga yankion Hong Kong, duba da irin ci gaban da yankin ya samu tun dawowarsa hannun kasar Sin a shekarar 1997.
Shugaba Xi wanda har ila shi ne babban sakataren kwamitin tsakiyar JKS ya bayyan hakan ne lokacin da ya ziyarci dakin adana kayan tarihi na kasa dake Beijing, inda aka baje kolin tarin nasarorin da aka cimma a yankin cikin sama da shekaru 20 da suka gabata.(Ibrahim)