in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan yankin Hong Kong sun sha alwashin aiwatar da dokar aikin 'yan majalissu
2016-11-07 14:12:50 cri
Babban jami'in gudanarwar yankin Hong Kong na kasar Sin Leung Chun-ying, ya ce sashen zartaswa da na majalissar yankin musamman na Hong Kong ko (SAR) a takaice, za su tabbatar da cikakken goyon bayan su wajen aiwatar da dokar aikin 'yan majalissu mai lamba ta 104, wadda ta tanaji cikakkiyar biyayya ga muhimmiyar dokar aikin majalissa.

Mr. Leung wanda ya bayyana hakan a Litinin din nan, bayan da babban kwamitin zartaswa na JKS ya zartas da wannan doka da safiyar yau din, ya kara da cewa ba za a lamunci duk wani yunkuri na karya dokar, ko cin zarafin kasar Sin ba, kuma duk wanda ya karya wannan doka zai fuskanci fushin hukuma.

Fashin bakin wannan doka dai ya tanaji martaba dokokin yankin Hong Kong na musamman na kasar Sin, tare da amincewa da dokokin yankin na Hong Kong na kasar Sin. Bayan haka kuma, tanajin dokar ya hada da rantsuwar martaba ka'idojin dokar, ciki hadda na tsayawa takarar zabuka wanda dokar ta fayyace.

Rahotanni dai sun bayyana cewa zababbun 'yan majalissar dokokin yankin na Hong Kong ta 6 su biyu, sun furta kalaman rashin martabawa ga kasar Sin da gangan, lokacin da suke rantsuwar kama aiki a ranar 12 ga watan Oktobar da ta gabata. Sai dai jami'in lura da rantsuwar kama aikin na su, bai amince da rantsuwar da suka yi ba. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China