in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi Allah wadai da harin da aka kai Mali
2017-06-21 13:18:34 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi Alllah wadai da harin ta'adancin da aka kai kan wani otel dake wajen birnin Bamakon kasar Mali, harin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla biyar.

Guterres wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, ya kuma bayyana kudurin MDD na ci gaba da taimakon gwamnati da al'ummar kasar Mali da kungiyoyi masu dauke da makamai da suka sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiyar kasar, a kokarin da suke yi na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar, ta hanyar yakar ayyukan ta'addanci da tsattsauran ra'ayi.

Bugu da kari, Guterres ya aike da sakon ta'aziya ga gwamnati da iyalan wadanda suka rasa rayukansu sanadiyar wannan hali, tare da fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China