in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya ba za ta kori 'yan gudun hijirar Afirka da suka shigo cikin kasar ba
2017-06-20 10:17:28 cri
Mahukuntan kasar Aljeriya sun sanar da cewa, ba za su tusa keyar bakin hauren Afirka da suka shigo cikin kasar ba.

Kamfanin dillancin labaran kasar na APS ya ruwaito ministan harkokin cikin kasar Noureddine Bedoui na cewa, kasar ta Aljeriya tana daukar 'yan gudun hijira da mutanen da rikici a kasashensu ya raba da muhallansu a matsayin bakin ta.

Bedoui ya ce, hukumomi na sane da halin da 'yan gudun hijirar ke ciki musamman mata da kananan yara, kuma gwamnati na duba yiwuwar samar wa 'yan gudun hijirar aikin yi, musamman a fannin gine-gine.

Daruruwan Dubban 'yan gudun hijira gilibi daga kasashen Nijar, Chadi, Mali da Syria da Libya ne ke zauna a cikin kasar Aljeriya, sakamakon yakin da ake gwabzawa a kasashensu.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China