in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Tunisia da Algeria sun cimma yarjeniyoyi da dama yayin Babban taron hukumar kawancen kasashen biyu
2017-03-10 11:02:24 cri
Firayiministan Algeria Abdelmalak Sellal da takwaransa na Tunisia Youssef Chahed da suka jagoranci babban taron hukumar kawacen kasashen biyu karo na 21, sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi da dama a tsakaninsu.

Yayin taron da ya gudana jiya Alhamis, kasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi 9 a bangarorin da suka shafi tattalin arziki da tsare-tsare da fasahohi da kuma cinikayya.

Har ila yau, kasashen sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna ta fuskar kare hakkin masu sayan kayayyaki da kuma tabbatar da ingancin kayayyaki da ayyuka.

Firayiministan Algeria Abdelmalak Sellal, ya ce hadin gwiwa tsakanin kasashen Algeria da Tunisia a bangarori da dama, alama ce dake nuna karfin dangantakar dake tsakaninsu, yana mai alakanta nasarar da kyakkyawar huldar dake tsakanin shugabannin kasashen wato Abdelaziz Boutaflika na Aljeria da takwaransa na Tunisia Beji Caid Essebsi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China