in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan kasashen BRICS na fatan bunkasa hadin gwiwar kungiyar a shekaru 10 masu zuwa
2017-06-16 12:44:07 cri
Wakilan shugabannin kasashen BRICS mashirya tarunkan kungiyar, sun amince da daukar matakan karfafa hadin gwiwa, tsakanin kasashe mambobin kungiyar cikin shekaru 10 masu zuwa.

Wakilan sun gabatar da wannan kuduri ne a jiya Alhamis, yayin taro karo na biyu na kwanaki biyu da suka gudanar a birnin Qingdao na lardin Shandong dake gabashin kasar Sin.

Mahalarta taron sun yi bitar nasarorin da aka samu a fannin hadin gwiwar kasashe mambobin kungiyar ta BRICS, musamman a fannonin siyasa, da tsaro, da tattalin arziki, tare da musaya ta al'adu da jama'a tsakanin sassan kasashe mambobin ta.

Sun kuma nazarci shirye shirye da ake gudanarwa, game da taron kungiyar na bana, wanda ke tafe tsakanin ranekun 3 zuwa 5 ga watan Satumba a birnin Xiamen dake lardin Fujian.

Mahalarta taron sun kuma jinjinawa kasar Sin, game da jagoranci managarci da take baiwa BRICS, yayin da take rike da kujerar karba karba ta shugabancin kungiyar a bana, sun kuma tabbatar da aniyar su, ta marawa kasar baya, a yunkurin cimma nasarar taron birnin na Xiamen wanda ke tafe nan da 'yan watanni. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China