in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in diflomasiyyar kasar Sin bayyana muhimmancin samar da kyakkyawar makoma ga al'umma wajen kare hakkokin dan adam
2017-06-15 10:52:33 cri
Shugaban tawagar wakilin kasar Sin na MDD a Geneva Ma Zhaoxu, ya ce ya kamata kasashe su yi aiki tare wajen gina al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil'adama, domin inganta muradin kasashen duniya na kare hakkin dan adam.

Ma Zhaoxu ya yi wannan bayani ne yayin taron kasashen duniya kan hakkokin dan Adam da samar da kyakkyawar makoma na bai daya, wanda cibiyar kare hakkin dan Adam ta kasar Sin da shirin kasar Sin na MDD a Geneva suka shirya.

A cewar babban jami'in, samar da daidaito tsakanin yankuna shi ne tubalin inganta kare hakkin dan Adam, kuma dole ne dukkan bangarori su kare hakkokin dan Adam tare da tabbatar da hadin kai a matsayin 'yan uwan juna da kuma yi wa manufofin kare hakkokin dan Adam na sauran kasashe kyakkyawar fahimta.

Ma ya kuma jadadda muhimmanci damawa da kowa tare da koyo daga juna yana mai cewa ita ce muhimmiyar hanyar kare hakokin bil'adma.

Har ila yau, ya ce kamata ya yi al'ummomin duniya su girmama bambancin wayewar kan bangarori daban-daban ta yadda zai tafi kafada-da-kafada da zaman lafiya tare da koyi da juna. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China