in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Qatar a shirye take da tattauna da kasashen yankin Gulf: in ji ministan wajen Kuwait
2017-06-12 10:13:57 cri
Ministan harkon wajen Kuwait Sabah Al-Khaled Al-Hamad Al-Sabah ya bayyana cewa Qatar a shirye take ta fahimci juna tsakaninta da takwarorinta kasashen yankin Gulf kuma za ta tattauna da su domin kawo karshen zaman tankiya dake ci gaba da wanzuwa tsakaninsu.

Kamfanin dillancin labarai na KUNA ya ruwaito ministan harkokin wajen Kuwaitin cewa, kasar Qatar a shirye take ta tattauna da kasashen domin lalibo bakin zaren warware sabanin dake tsakaninsu, kuma za ta karfafa dukkan matakai da za su tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.

Sanarwar ta zone bayan da kasashen yankin Gulf din da suka hada da Saudi Arabia, Hadaddiyar daular Larabawa (UAE) da Bahrain, da kuma kasar Masar, har ma da sauran kasashen da ba na yankin Gulf din ba, suka zargi Qatar da hannu wajen taimakawa kungiyoyin 'yan ta'adda da kuma yin katsalandan cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe.

Cikin majalisar hadin kan kasashen 6 na yankin Gulf (GCC), Kuwait da Oman ne kadai ba su bi sahun takwarorinsu ba, wajen yanke hulda da Qatar, kuma shugabannin Kuwait na ci gaba da tattunawa da bangarorin da abin ya shafa domin lalibo bakin zaren kawo karshen takaddamar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China