in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: Al'ummun Afirka miliyan 20 na fuskantar matsalar fari
2017-05-19 10:11:38 cri
Kimanin al'ummun wasu kasashen Afirka hudu su miliyan 20 ne ke fuskantar matsalar fari, sakamakon kalubalen karancin ruwan sama, da kuma tashe tashen hankula masu nasaba da kungiyoyin 'yan ta'adda.

Da take tabbatar da hakan yayin wani taron manema labarai, darakta a ofishin shirin abinci na duniya Denise Brown, ta ce yawan mutane da ke kara tsunduma cikin wannan matsala na karuwa, musamman a arewa maso gabashin Najeriya, da kasar Somalia, da Sudan ta kudu, da kuma Yemen. Ta ce tasirin wannan matsala lamari ne mai tada hankali, irin wanda ba a taba ganin irin sa a baya ba.

A nasa bangare, darakta mai kula da harkokin gaggawa da ayyukan farfado da yankuna, a hukumar abinci da ayyukan gona na MDD FAO Dominique Burgeon, ya ce tashe tashen hankula, da matsalar sauyin yanayi na hallaka dabbobi, tare da rage kyawun filayen noma, a gabar da kuma kusan kaso 80 bisa dari na al'ummar wadannan yankuna ke dogaro kan wadannan albarkatu.

Mr. Burgeon ya kara da cewa, idan har ba a dauki matakan da suka kamata ba, ana iya fuskantar fari irin wanda aka gamu da shi a tsakanin shekarar 2010 zuwa 2011 a Somalia, wanda a wancan lokaci ya sabbaba rasa rayukan mutane 250,000. Ya ce hakan ya faru ne, sakamakon yadda kasashen duniya suka yi biris da lamarin.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China