in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya za ta samar da hanyoyin ruwa a Kogin Niger domin noman rani
2017-06-07 10:02:59 cri
Ministan albarkatun ruwa na Nijeriya Suleiman Adamu, ya ce an fara shirin samar da ingantattun hanyoyin ruwa domin noman rani a kogin Niger

Suleiman Adamu wanda ya bayyana haka a jiya Talata, ya ce za a aiwatar da aikin ne da hadin gwiwar gwamnatin Hungary domin lalubo yadda za a samar da kariya da zai kare bakin koguna da yankunan koguna da ke fuskantar ambaliyar ruwa.

Ministan ya ce duk da muhimmin aikin zai dauki lokaci, ma'aikatar ta fara tattaunawa da masana daga kasar Hungary.

Kogin mai nisan kilomita 4,280 da fadin murabba'in kilomita miliyan 2.2, ya samo asali ne daga yankin Faranah na kudu maso gabashin Conakry, inda ya ratsa ta kasashen Afrika da suka hada da Guinea da Mali da Niger da Benin da kuma Nijeria, ya kuma dangana zuwa tekun Atlantika.

Suleiman Adamu ya ce ma'aikatarsa za ta samar da kudin aiwatar da aikin ne da hadin gwiwar bangarori masu zaman kansu, yana mai jadadda cewa, ya kamata a ce Nijeriya tana da yankuna noman rani ba tare da fuskantar barazanar ambaliya ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China