in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNFPA ya baiwa 'yan matan Chibok gudummawar wasu kayayyaki
2017-06-03 12:25:53 cri
Asusun kula da yawan al'umma na MDD (UNFPA) a takaice ya ce, yana kokarin taimakawa 'yan matan sakandaren Chibok da aka ceto daga hannun mayakan Boko Haram a Najeriya, ta yadda za su sake komawa cikin al'umma don ci gaba da gudanar da harkokinsu na rayuwa.

Mataimakiyar wakiliyar asusun a Najeriya Eugene Kongnyuy ce ta bayyana hakan a Abuja lokacin da take mika wasu kayayyakin kula da lafiya ga 'yan matan na Chibok 106 da aka ceto wadanda a halin yanzu ke cibiyar gyaran tunani.

Ta ce asusun ya samar da wadannan hidimomi ga yaran ne tare da taimakon wasu abokan hulda gami da kokarin gwamnatin tarayya da na jihohin kasar.

Kayayyakin da asusun ya baiwa 'yan matan na Chibok sun hada da kayayyakin sakawa na gargajiya da 'yan kwalaye, kananan wanduna ko kamfai, audugun mata, sabulu, man goge baki da tawul din wanka. Haka kuma asusun ya himmantu wajen ganin an dawo da martaba da kimar 'yan matan da aka ceto.

A nata jawabin yayin bikin ministar mata da walwalar jama'a ta Najeriya, Aisha Alhassan ta bayyana cewa, gwamnati ta yi na'am da irin taimakon da asusun ke bayarwa, musamman wajen farfado da kayayyakin dake cibiyar da aka tsugunar da 'yan matan da biyan kudaden albashin ma'aikatan da ke kula da su da kayayyakin amfanin yau da kullum da kuma dabarun gyara tunani. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China