Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana a yau Laraba yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing cewa, kasar Sin ta yi tir da harin bam din da aka kai a yankin ofisoshin jakadancin kasashen waje da ke birnin Kabul, hedkwatar kasar Afghanistan a wannan rana da safe.
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta Afghanistan ta ce, mutane 80 sun rasa rayukansu sakamakon harin bam din, yayin da wasu 320 kuma suka jikkata. (Tasallah Yuan)