in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta nuna damuwa kan yadda rikici ya yi kamari a Afghanistan
2017-04-24 20:06:58 cri

A yau Litinin ne Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, kasar Sin tana damuwa sosai kan yadda rikici ya ke kara kamari a kasar Afghanistan.

Mista Geng ya fadi haka ne yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing. A ranar 21 ga wata da yamma ne, aka kaiwa hari wani sansanin soja na rundunar tsaron Afghanistan dake a lardin Balkh na kasar, inda mutane a kalla 140 suka rasa rayukansu ya zuwa yanzu. 'Yan tawayen Taliban sun yi shelar daukar alhakin kai harin. Yayin da mista Geng ya amsa tambayar da ke shafar lamarin, ya bayyana cewa, kasar Sin ta yi kira ga sassa daban daban na Afghanistan da su hau teburin sulhuntawa karkashin jagorancin al'ummar Afghanistan, a kokarin kiyaye zaman lafiya da ci gaban kasar ta Afghanistan. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China