Haka zalika, shugaban na kasar Sin ya ce kasarsa ba ta goyon bayan kowane irin aikin ta'addanci, don haka ya yi Allah wadai da wadanda suka kai wannan mummunan hari da kakkausan harshe.
Har ila yau, Shugaba Xi ya ce a ko da yaushe, kasar Sin ta na goyon bayan kasar Masar kan kokarin da take na kiyaye tsaro da dakile ta'addanci.
Shi ma a nasa bangaren, firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya aike da sakon ta'aziyya ga takwaransa na kasar Sherif Ismail.(Bello Wang)