in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da firaministan kasar Habasha
2017-05-12 18:32:31 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da Hailemariam Dessalegn, firaministan kasar Habasha, wanda ke birnin Beijing domin halartar taron dandalin koli na hadin gwiwar kasa da kasa karkashin shawarar "ziri daya da hanya daya", wanda zai gudana tsakanin ranekun 14 zuwa 15 ga wannan wata.

A cewar shugaban kasar Sin, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Habasha ta riga ta zama kan gaba a hadin gwiwar da ake yi tsakanin bangarorin Sin da Afirka. Don nuna muhimmancin huldar dake tsakanin kasashen 2, da matsayin da suka cimma a fannin amincewa da juna, shugaban kasar Sin ya ba da shawarar daga matsayin huldar dake tsakanin kasashen 2, zuwa irin abokantakar da ta shafi hadin gwiwa ta fuskar manyan tsare-tsare.

Shugaban ya kara da cewa, kasar Sin ta taya ma kasar Habasha murnar shiga cikin jerin mambobin bankin zuba jari ga kayayyakin more rayuwa na Asiya, kuma za ta ci gaba da goyon bayan kasar Habasha domin ta taka rawar hada nahiyar Afirka da sauran nahiyoyi bisa shawarar "ziri daya da hanya daya"

A nasa bangaren, firaministan kasar Habasha, Hailemariam Dessalegn, ya ce shawarar "ziri daya da hanya daya" tana da ma'ana mai zurfi ga duniya, kuma ta nuna hangen nesa da sanin ya kamata. Wannan shawara a cewar shugaban, za ta taimakawa hada yankuna daban daban na duniya, da karfafa hadin gwiwa a fannin cinikayya da zuba jari. Saboda haka, kasar Habasha ta yi kokarin halartar ayyukan hadin kai da ake yi karkarshin laimar shawarar "ziri daya da hanya daya".(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China