in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta zargi lamarin kai farmaki kan motocin safa a Masar
2017-05-27 12:46:41 cri
Kwamitin sulhun MDD da babban sakataren Majalisar Antonio Guterres sun yi tir da farmaki kan motocin safa da wasu 'yan bindiga suka kai a lardin Minya na kasar Masar, suna masu bukatar a tabbatar da hukunta maharan. Cikin wata sanarwar da kwamitin sulhun ya fitar a jiya, ya jaddada cewa, ko wane irin nau'i na ta'addanci kalubale ne mai tsanani ga zaman lafiya da tsaro na duniya.

Kwamitin ya kuma kalubalanci dukkan kasashe su hada kai da Masar wajen yaki da ayyukan ta'addanci bisa dokokin kasa da kasa da kudurorin kwamitin sulhun.

Shi ma a nasa bangare, Antonio Guterres ya bayar da sanarwa ta bakin kakakinsa cewa, babu wani dalili da zai sa a kai irin wannan farmaki na ban mamaki.

Ya kuma nuna juyayi tare da jajantawa iyalan mutanen da suka mutu, da gwammati da jama'ar kasar ta Masar, tare kuma da bayyana fatan sa na ganin wadanda suka ji rauni sun samu sauki cikin gaggawa.

Hukumomin tsaron kasar Masar sun ba da labarin cewa, wasu 'yan bindiga da ba a san asalinsu ba, sun kai farmaki a jiya Juma'a, kan wasu motocin safa biyu masu dauke da mabiya addinin Krista a yankin Minya dake kudancin kasar.

Rahoton gidan talibijin na kasar ya ruwaito cewa, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane a kalla 28, tare da jikata wasu 25. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China