in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani hari a Masar, ya yi sanadin mutuwar dan Sanda daya tare da jikkata wasu mutane hudu
2017-04-19 10:23:45 cri
Gidan Talabijin na Masar ya ruwaito cewa, akalla dan sanda daya ne ya rasa ransa yayin da wasu mutane hudu suka jikkata, a wani hari da aka kai shingen bincike dake kusa da Mujami'ar St. Catherine a kudancin Sinai.

Jaridar Ahram ta kasar ta wallafa a shafinta na Intanet cewa, wasu mahara da ba a san ko su waye ba, sun kai farmaki shingen binciken jami'an tsaro, amma babu abun da ya samu limaman dake cikin mujami'ar.

An dai garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibitin Sham El-Sheikh.

Wannan harin na zuwa ne kwanaki bayan an kai hare-hare biyu kan wasu mujami'u a kasar, alamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 47, kuma kungiyar IS ta dauki alhakinsa.

Masar dai na fama da hare-hare kan jami'an tsaro a yankin arewacin Sinai, inda Kungiyar IS ta fi kai farmaki, al'amarin da ya hallaka daruruwan jami'an tsaro. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China