in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in kasar Sin ya yi kira da a kara yin hadin kai a fannin yakar ta'addanci
2017-05-25 20:05:00 cri
A jiya Laraba ne babban sakatare mai kula da shari'a da tsaron jama'a na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mista Meng Jianzhu, ya bayyana cewa gwamnatin kasar sa na adawa da duk wani nau'in aikin ta'addanci, kuma ta dade tana neman ganin a yi hadin gwiwa a fannin ayyukan 'yan sanda na kasashe daban daban.

Mr. Meng ya ce bisa la'akari da yanayi mai tsanani da ake ciki a fannin yaki da ta'addanci, kasar Sin na fatan ganin kafuwar wani tsarin hadin kai ta fuskar yakar ta'addanci wanda ke yaduwa cikin sauri ta hanyar yanar gizo ko Internet.

Mr. Meng ya yi wannan tsokaci ne yayin wani taron manyan kusoshi a fannin aikin tsaro wanda aka kira a kasar Rasha, ya ce a bisa tsarin hadin gwiwa ne za a kara hada karfi waje guda don samun kwanciyar hankali a duniya, da tabbatar da tsaron jama'ar kasashe daban daban, da yunkurin dakile ta'addanci.

Taron dai ya samun halartar wakilai na kasashe da kungiyoyi 95.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China