in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Amurka ya ce zai kara kasafin kudin tsaron kasar
2017-02-28 13:48:32 cri

Shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya shaidawa taron kungiyar gwamnonin jihohin kasar cewa, zai karawa bangaren tsaron kasar kudade a kasafin kudin da zai gabatarwa majalisar dokokin kasar, a yunkurin farfado da karfin sojan kasar.

Kafofin yada labarai na kasar Amurka a wannan rana sun ruwaito wani jami'in sashen kula da harkokin kasafin kudi na fadar White House yana cewa, Mr. Trump na shirin kara kashi 10 cikin 100 na kudin da za a kasaftawa fannin tsaro, wato kimanin dala biliyan 54, a yayin da za a rage kudin a wasu fannonin da ba su shafi harkokin tsaro ba, misali fannin samar da taimako ga kasashen waje. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China