in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi shawarwari tsakanin ministocin harkokin waje na kasashen Sin da Mauritania
2017-05-20 13:41:16 cri
Baya ga ganawa da shugaban kasar Mauritania yayin ziyarar da yake a kasar, ministan harkokin wajen Sin Wang Yi ya kuma gana da takwaransa na kasar Isselkou Ould Ahmed Izid Bih a Nouakchott.

Yayin ganawar da ta gudana a jiya, Wang yi ya bayyana kasashen Sin da Mauritania a matsayin kawayen juna. Inda ya ce kasancewar Mauritania mamba a dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, da kuma dandalin tattaunawa tsakanin Sin da kasashen Larabawa, tana iya amfani da wadannan dandamalin biyu wajen karfafa hadin kai da kasar Sin a dukkan fannoni, kuma Kasar Sin ta yi imanin cewa Mauritania na da kyakkyawar makoma.

Baya ga haka, ministan harkokin wajen na Sin ya bayyana cewa, har kullum kasar Sin na goyon bayan kasashen Afirka wajen warware matsalolinsu da kansu, inda ta ke goyon bayan muhimmiyar rawar da kungiyoyin shiyyar ke takawa kan harkokin da suka shafi kasashensu.

A nasa bangaren, mista Izid Bih ya bayyana cewa, kasar Mauritania na son koyi da fasahohin da Sin ta yi amfani da su wajen samun ci gaba, tare kuma da karfafa hadin kai da moriyar juna a fannoni daban- daban.

Baya ga haka, ministocin biyu sun yi musayar ra'ayoyi kan muhimman batutuwan da suka shafi nahiyar Afirka. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China