in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu mutane 5 sun mutu sakamakon harin bom a Mogadishu
2017-05-09 13:40:56 cri
An kai harin mota a Mogadishu, hedkwatar kasar Somaliya, a jiya Litinin, inda mutane 5 suka mutu, ciki har da wani babban hafsan sojojin kasar.

Sanarwar da 'yan sandan kasar suka bayar ta nuna cewa, wata mota mai dauke da boma-bomai ta kutsa kai cikin wani wurin cin abincin irin na Italiya, sa'an nan ta fashe, al'amarin da ya haddasa mutuwar mutane 5, tare da raunata wasu 10.

Ana fargabar adadin wadanda suka mutu zai karu, la'akari da raunuka masu tsanani da wasu mutane suka samu.

Kungiyar Al-Shabab ta masu tsattsauran ra'ayi, wadda ke da alaka da kungiyar ta'addanci ta Al-Qaeda, ta sanar da daukar alhakin wannan hari.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China