in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ce kasashen Sudan ta Kudu da Somalia na cikin matsananciyar yunwa
2017-04-19 09:40:50 cri
Shugaban sashen ayyuka na ofishin kula da agajin jin kai na MDD John Ging, ya ce yankin arewa maso gabashin Afrika na fuskantar rikici da ka iya jefa kasashen Somali da Sudan cikin matsanancin karancin abinci.

John Ging, ya ce yayin da Somalia ke tunkarar matsalar a yanzu, Sudan ta kudu ba ta iya wa.

Jami'in ya bayyana haka ne jiya Talata a hedkwatar MDD dake birin New York, lokacin da yake yi wa manema labarai bayani game da rangadin gaggawa da ya kai kasashen.

Ya ce matsalar karancin abinci ta yi kamari a kasashen, ya na mai cewa kimanin mutane miliyan 6.2 ne ke bukatar agajin jin kai a Somalia, kuma saboda rikici da ake fama da shi, an samu barkewar cutar amai da gudawa, inda mutane 25,000 suka kamu da ita. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China