A cewar 'yan sandan kasar, fashewar ta abku ne a garin Glgala dake yankin Puntland. Kuma ga alama an tsara lamarin ne musamman domin hallaka sojojin gwamnatin dake wurin, wadanda ke kokarin dakile masu tsattsauran ra'ayi na kungiyar Al-Shabab.
A nata bangare, kungiyar Al-Shabab ta dau alhakin kai wannan hari, bayan abkuwar sa.
Don kau da kungiyar Al-Shabab, wadda ke da alaka da kungiyar ta'addanci ta Al-Qaida, sojojin gwamnatin kasar Somaliya, da hadin gwiwar sojojin kungiyar tarayyar Afirka AU, sun gudanar da jerin matakan soja a kasar Somaliya. (Bello Wang)