in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Barkewar cutar Kwalara ya yi sanadin mutuwar mutane 618 a Somalia tun daga farkon shekarar nan
2017-05-05 10:11:58 cri
Hukumar bada agajin jin kai ta MDD, ta ce barkewar cutar amai da gudawa mai tsanani a Somalia, ya yi sanadin mutuwar mutane 618 tun daga watan Junairun bana.

A rahotonsa na baya-bayan nan, ofishin kula da harkokin bada agajin jin kai na MDD, ya ce cutar ta barke ne a yankuna 13 daga cikin 18 dake kasar Somalia.

Ya kuma alakanta barkewar cutar da matsalar karancin ruwa da abinci da gudun hijira, da ya jefa tabbatar da tsafta cikin wani hali.

Hukumar ta ce kusan mutane 32,000 ne suka yi fama da cutar, inda kuma 618 suka mutu tun daga farkon shekarar 2017.

Ta ce yara da manya dake kokarin rayuwa cikin matsalar rashin abinci da sinadarai masu gini jiki, wanda fari a bara ya haifar, su ne suka kamu da cutar sanadiyyar shan ruwa mara tsafta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China