in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da sakin 'yan mata 82 da aka yi garkuwa da su a Nijeriya
2017-05-09 11:16:52 cri
Kakakin MDD Stéphane Dujarric, ya ce Majalisar ta yi maraba da sakin 'yan mata 82 da kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da su a Nijeriya.

Dujarric ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai a jiya, inda ya ce MDD ta damu da lafiya da tsaron 'yan matan da aka saki da kuma wadanda har yanzu ake ci gaba da garkuwa da su, tana mai kira ga iyalan wadanda aka saki da dukkan al'umar kasar, su karbe su, su kuma ba su kwarin gwiwar sake gudanar da rayuwarsu kamar da.

Dujarric ya kara da cewa, MDD ta yi kira ga kasashen duniya su ci gaba da nuna goyon baya ga gwamnatin Nijeriya don tabbatar da sakin dukkan mutanen da kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da su tare da sake shigar da su cikin zamantakewar al'umma.

A daren ranar 6 ga watan nan ne, Jami'in gwamnatin Nijeriya ya tabbatar da cewa, an saki 82 daga 'yan matan Sakandaren Chibok da kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da su a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China