in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan kasar Faransa da aka sake shi ya isa birnin Khartoum dake kasar Sudan
2017-05-08 16:26:09 cri
A jiya 7 ga wata aka sako dan kasar Faransa wanda aka yi garkuwa da shi a gabashin kasar Chadi a watan Maris na bana, kuma ya isa birnin Khartoum dake kasar Sudan a wannan rana.

Wannan dan kasar Faransa yana cikin lafiya yayin da yake isa filin jiragen saman birnin Khartoum, kuma ya bayyanawa 'yan jarida a filin jirgin saman cewa, ya nuna godiya ga bangarorin da abin ya shafa da suka yi kokari wajen cetonsa.

Bisa labarin da fadar shugaban kasar Faransa da kafofin watsa labaru na kasar Faransa suka bayar, an ce, wannan dan kasar Faransa ya taba yin aiki a wani kamfanin hakar ma'adinai, an yi garkuwa da shi ne a gabashin kasar Chadi kuma an kai shi zuwa kasar Sudan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China