in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta gargadi sassan Sudan ta Kudu da su kauracewa far wa juna
2017-05-01 12:44:53 cri
Kungiyar hadin kan kasashen Afirka ta AU, ta ja hankalin sassan kasar Sudan ta kudu da su kauracewa daukar matakan tada husuma a jaririyar kasar.

Shugaban hukumar zartaswar kungiyar Moussa Faki Mahamat, shi ne ya yi wannan kira, cikin wata sanarwa da aka fitar a jiya Lahadi. Mr. Mahamat ya ce kamata yayi tsagin gwamnatin hadin kan kasar da na 'yan adawa, su daina kaiwa juna farmaki, musamman ma a yankin jihar Upper Nile inda al'amura suka fi ta'azzara.

Ya ce tashe tashen hankula dake faruwa a kasar, na ci gaba da haifar da koma baya a fannin tsaron kasa, tare da barazana ga rayukan al'ummar kasar baki daya.

Daga nan sai ya bukaci dukkanin sassan da ba sa ga maciji da juna, da su martaba dokokin kasar, da ma yarjejeniyar da aka cimma game da warware rikicin siyasar Sudan ta kudun.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China