in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Da sanyin safiyar yau aka bude rumfunan zabe don jefa kuri'u a zagaye na 2 na zaben shugaban kasar Faransa
2017-05-07 17:39:25 cri
Tun da sanyin safiyar yau Lahadi ne aka bude rumfunan zabe a biranen kasar Faransa domin zabar wanda zai ja ragamar shugabancin kasar a zagaye na biyu na zaben tsakanin ɗan takara mai matsakaicin ra'ayi, Emmanuel Macron, da kuma mai tsaurin ra'ayin kishin ƙasa Marine Le Pen.

Sama da rumfunan zabe 66,000 ne aka bude don jefa kuri'u a fadin kasar ta Faransa, kuma an bude rumfunan zaben ne tun da misalin karfe 8 na safe agogon kasar wato karfe 6 agogon GMT, kuma an tsara gudanar da zaben har zuwa karfe 8 na dare wato karfe 6 na yamma agogon GMT a manyan biranen kasar, amma a sauran yankunan kasar za a rufe rumfunan zaben ne da misalin karfe 7 na yamma agogon kasar wato karfe 5 na yamma agogin GMT.

A kalla mutane miliyan 47 ne ake sa ran za su kada kuri'un su a lokacin zaben na yau Lahadi.

Sai dai da ma tuni Faransawa mazauna ketare suka kada nasu kuri'un tun a jiya Asabar, amma ba za'a fadi sakamakon zaben ba sai an kammala zaben a duk fadin kasar baki daya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China