in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar tattalin arziki da ciniki a tsakanin Sin da Uganda
2017-05-07 12:58:57 cri
A kwanakin baya, aka gudanar da taron dandalin tattauna hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasar Sin da kasar Uganda karo na farko a babban birnin kasar Uganda, Kampala, inda mahalarta taron suka tattauna game da yadda za a raya ayyukan samar da ababen more rayuwa da masana'antu a kasashen Afirka.

Kungiyar kasuwanci ta kasar Sin dake kasar Uganda da hukumar zuba jari ta kasar Uganda suka gudanar da taron cikin hadin gwiwa, haka kuma, mataimakin shugaban kasar Uganda Edward Ssekandi, da wasu jami'an ma'aikatar harkokin kudi, da jakadan kasar Sin dake kasar Uganda Zheng Zhuqiang, da wasu wakilan kamfanonin kasar Sin masu zaman kansu dake kasar Uganda sun halarci wannan taro.

A yayin taron, Mr.Ssekandi ya bayyana cewa, domin cimma burin kasar na 2024, a 'yan shekarun nan, kasar Uganda ta dukufa wajen raya ababen more rayuwa, a nan gaba kuma za ta mai da hankali kan raya harkokin masana'antu. Bugu da kari, kasarsa za ta ci gaba da kyautata yanayin zuba jari a kasar, da aiwatar da shirin hadin gwiwar Sin da Afirka yadda ya kamata, shi ya sa, kasar Uganda take fatan samun karin taimako da goyon baya daga bangaren kasar Sin domin karfafa bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'ummar kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China